Episode description
Adisu Abba wata mata ce mai shekaru 45 kuma uwa ga ‘ya’ya biyar. Ta fito daga Dikwa, Jihar Borno, a arewa maso gabashin Najeriya. Tun kafin rikici ya tarwatsa rayuwarta, ta riga ta fara koyon aikin da zai zama ginshiƙin rawarta a cikin al’ummarta—ta koyi yadda ake taimaka wa mata wajen haihuwa.
An yi garkuwa da Adisu a hannun ‘yan ta’adda na tsawon shekaru uku,a wannan lokacin, ta taimaka wajen haihuwar jarirai biyar.
A wannan shirin na #BIRBISHINRIKICI, mun bada labarinta da kuma abin da yake nufi yin aikin ungozoma yayin da take tsare a hannun ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram.
Support Our Journalism
There are millions of ordinary people affected by conflict in Africa whose stories are missing in the mainstream media. HumAngle is determined to tell those challenging and under-reported stories, hoping that the people impacted by these conflicts will find the safety and security they deserve.
To ensure that we continue to provide public service coverage, we have a small favour to ask you. We want you to be part of our journalistic endeavour by contributing a token to us.
Your donation will further promote a robust, free, and independent media.
